Gwamnatin Tarayya ta sanar da fara gyaran tituna a Najeriya
Ministan ayyuka na Najeriya, David Umahi, ya roƙi ‘yan Najeriya da su fara shirin bibiyar ayyuka na gina hanyoyi waɗanda za a fara yi a faɗin ƙasar nan.
Ministan ayyuka na Najeriya, David Umahi, ya roƙi ‘yan Najeriya da su fara shirin bibiyar ayyuka na gina hanyoyi waɗanda za a fara yi a faɗin ƙasar nan.
Kungiyar ‘Yan Kasuwa, Masana’antu, Ma’adanai, da Noma ta Kano, KACCIMA, ta ce tana shirin sanyawa cibiyar kasuwanci da taro da sunan Shugaban Kamfanin Dangote Group, Aliko Dangote.
Hajiya Aisha Ibrahim Bura ta lashe zaben shugabancin Kungiyar mata ‘yan jarida wato NAWOJ ta kasa, wanda aka gudanar a Birini taraiyya Abuja.
Ƙungiyar Ƙwadago ta Najeriya da soki gwamnatin tarayya kan rage yawan kuɗin da ta ware domin biyan albashi ga ma’aikatan gwamnati zuwa Naira biliyan 100 a cikin ƙarin kasafin kudi da gwamnatin ta yi.
Ƙungiyar da ke yaƙi da safara da bautar da ƙananin yara NACTAL tare da haɗin guiwa da hukumar yaƙi da safarar bil’adama ta ƙasa NAPTIP, da sauran kwamitocin karta kwana da ke yaƙi da wannan ɗabi’a, sun gudanar da taron wuni ɗaya domin wayar da kan al’umma kan matsalolin safar bil’adama da shigi da fici ba bisa ƙa’ida ba a nan jihar Kano.
Rukuni na hudu, ɗauke da ɗalibai 150 da gwamnatin Kano mai ci ta ɗauki nauyin karatunsu a ƙasashen waje sun tashi zuwa ƙasar India domin yin karatun digiri na biyu a fanni daban-daban.
A bayanan da Gwamnatin Jihar Kaduna ta samu ya nuna cewa sojojin sun fara aikin sintirin ta hanyar Kaduna-Sabon Birni-Dogon Dawa, har zuwa Maidaro da Ngede Allah, kafin su wuce yankin Saulawa da Kidandan.
A jiya Alhamis kotun ɗaukaka kara da ke zamanta a Abuja ta ayyana zaɓen gwamnan jihar ta Zamfara a matsayin wanda bai kammala ba. inda ta bayar da umarnin sake gudanar da zaɓe kananan hukumomi uku da suka haɗa da Maradun, Birnin-Magaji da Bukkuyum.
A yammacin jiya Alhamis, wata majiya ta ce Kwamishinan yada labarai na Kano, Alhaji Baba Halilu Dantiye ya yi wannan kira a wani jawabi da ya fitar, inda ya ce shawarar ta zama dole ne ganin cewa wasu bata-gari za su iya amfani da damar shari’ar zabe, su kawo rikici a Kano.
Kotun ɗaukaka ƙara da ke zaman a babban birnin tarayya Abuja ta bayyana tsohon mataimakin gwamnan jihar Kano, Nasiru Yusuf Gawuna kuma dan takarar APC a matsayin wanda yai nasara a zaben gwamnan jihar Kano da aka gudanar a ranar 18 ga watan maris da ya gabata.