Gwamnan Kano ya umarci muƙarrabansa su ajiye mukamansu a ranar 26 ga watan nan
Gwamnan jihar kano Abdullahi Umar Ganduje, ya bayar da umarni ga dukkanin Kwamishinoni da shugabannin Ma’aikatu da hukumomin gwamnatin kano da su ajiye mukamansu nan da ranar juma’a 26 ga wannan wata.










