DSS ta bayyana dalilanta na cigaba da tsare tsohon gwamnan babban banki, Godwin Emefiele
Hukumar tsaro ta farar kaya DSS, ta shaidawa babban kotun tarayya da ke zama a garin Abuja hikimar cigaba da tsare Godwin Emefiele.
Hukumar tsaro ta farar kaya DSS, ta shaidawa babban kotun tarayya da ke zama a garin Abuja hikimar cigaba da tsare Godwin Emefiele.
Gwamnan jihar Kano, Abba Kabir Yusuf ya amince da mayar da Barista Muhuyi Magaji Rimin Gado a matsayin Shugaban Hukumar Sauraron Korafe-korafen Al’umma da Yaki da Cin Hanci da Rashawa ta jihar Kano, domin kammala wa’adinsa.
Inda yaƙara da cewar, daga yanzu, duk wanda ya san sunansa ya shiga cikin waɗanda za’a naɗa kwamishina ya bayyana dukiyar da ya mallaka gabanin majalisa ta tantance shi.
Babbar Kotun Shari’ar Musulunci mai lamba 1 da ke Jihar Bauchi ta tura Dakta Idris Abdul’aziz Dutsen Tanshi gyara hali har zuwa nan da wata guda, bisa abin da ta kira ‘raini ga kotu’.
Kwamishinan ‘yansandan Jihar Zamfara, Muhammad Bunu, a madadin babban sufeton ‘yansanda na kasa, Usman Alkali Baba ya gabatar da check ɗin kudi na Naira miliyan 23,574,204 ga iyalai da ‘yan uwa 21 na jami’an ‘yansanda da suka rasa rayukansu a bakin aiki.
Gwamnan jihar Kano, Alhaji Abba Kabir Yusuf ya amince da nadin Yan kwamitin riko na hukumar gudanarwar kungiyar kwallon kafa ta Kano Pillars (Masu Gida).
majalisar dokokin jihar Kano ta nuna damuwa kan matsalolin satar waya da sane da shan miyagun kwayoyi da ma waɗansu laifukan da ke barazana ga zaman lafiyar jihar.
Gwamnan jihar Kano Engr. Abba Kabir Yusuf ya turawa Majalisar dokokin jihar kano sunayen mutane 19 domin tantancesu don nada su a matsayin kwamishinonin sa Kuma yan majalisar zartarwa jiha.
Shugaban kasa Bola Ahmed Tinubu, ya amince da yi wa dukkan hafsoshin tsaron Nijeriya da sufeto-Janar na ‘yan sanda da masu ba da shawara kan sha’anin tsaro da Kwanturola-Janar na Hukumar Kwastam murabus daga Ma’aikatunsu tare da maye gurbinsu nan take.
Tsohuwar Shugabar Kotun Daukaka Kara ta Najeriya Mai Shari’a Zainab Bulkachuwa ta musanta kalaman da mai gidanta ya yi na cewa ya yi amfani da damarsa, wajen nema wa abokan siyasarsa Sanatoci alfarma lokacin da take aiki a matsayin alkaliya.